Yohanna 8:3-5
3
Sai malaman dokoki da Farisiyawa suka kawo wata macen da aka kama a zina. Suka sa ta tsaya a gaban taron
4
suka kuma ce wa Yesu, “Malam, an kama wannan mace tana zina.
5
A cikin Doka Musa ya umarce mu, mu jajjefe irin waɗannan mata. To, me ka ce?”