Ayuba 39:9-12
9
“Ko ɓauna zai yarda yă zauna a wurin sa wa dabbobi abinci? Zai tsaya a ɗakin dabbobinka da dare?
10
Ko za ka iya daure shi da igiya a kwarin kunya? Zai yi maka buɗar gonarka?
11
Ko za ka dogara da shi don yawan ƙarfinsa? Za ka bar masa nauyin aikinka?
12
Ko za ka amince da shi yă kawo maka hatsinka gida yă tattara shi a masussuka?
Settings