Skip to content
Ayuba 23:1-7

Ayuba 23:1-7

1
Sa’an nan Ayuba ya amsa,
2
“Ko a yau, ina kuka mai zafi; hannunsa yana da nauyi duk da nishin da nake yi.
3
Da a ce na san inda zan same shi; da a ce zan iya zuwa wurin da yake zama!
4
Zan kai damuwata wurinsa in yi gardama da shi.
5
Zan nemi in san abin da zai ce mini, in kuma auna abin da zai ce mini.
6
Zai yi gardama da ni da ikonsa mai girma? Babu, ba zai zarge ni da laifi ba.
7
Mai adalci ne zai kawo ƙara a wurinsa, kuma zan samu kuɓuta daga wurin mai shari’an nan har abada.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options