Irmiya 29:5-6
5
“Ku gina gidaje ku zauna; ku dasa gonaki ku kuma ci abin da suka haifar.
6
Ku yi aure ku kuma haifi ’ya’ya maza da mata; ku nemi mata wa ’ya’yanku maza, ku kuma ba da ’ya’yanku mata ga aure, saboda su ma za su haifi ’ya’ya maza da mata. Ku riɓaɓɓanya a can, kada ku ragu.