Skip to content
Irmiya 22:28-30

Irmiya 22:28-30

28
Wannan mutum Yehohiyacin ne da aka rena, fasasshen tukunya, abin da babu wanda yake so? Me ya sa za a jefar da shi da ’ya’yansa a jefar da su a ƙasar da ba su sani ba?
29
Ya ke ƙasa, ƙasa, ƙasa, ki ji maganar Ubangiji!
30
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ka rabu da wannan mutum sai ka ce marar ’ya’ya, mutumin da ba zai yi nasara a rayuwarsa ba, gama babu zuriyarsa da za tă yi nasara babu wani da zai zauna a kursiyin Dawuda ko ya ƙara yin mulkin Yahuda.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options