Irmiya 13:15-16
15
Ku ji ku kuma saurara, kada ku yi girman kai, gama Ubangiji ya yi magana.
16
Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnku kafin ya kawo duhu, kafin ƙafafunku su yi tuntuɓe a kan tuddai masu duhu. Za ku sa zuciya ganin haske amma zai mai da shi duhu mai kauri ya kuma canja shi zuwa duhu baƙi ƙirin.