Skip to content
Irmiya 13:1-5

Irmiya 13:1-5

1
Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, “Tafi ka sayo abin ɗamara na lilin ka sha ɗamara da shi, amma kada ka bari yă taɓa ruwa.”
2
Saboda haka na sayo abin ɗamara, yadda Ubangiji ya umarce ni, na kuwa sha ɗamara da shi.
3
Sai maganar Ubangiji ta zo mini sau na biyu cewa,
4
“Ka ɗauki abin ɗamara da ka sayo, wanda ka ɗaura, ka tafi yanzu zuwa Fera ka ɓoye shi a cikin kogon dutse.”
5
Saboda haka na tafi na ɓoye shi a Fera, yadda Ubangiji ya ce mini.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options