Yaƙub 2:17-20
17
Haka ma bangaskiya ita kaɗai, in ba tare da ayyuka ba, matacciya ce.
18
Amma wani zai ce, “Kai kana da bangaskiya; ni kuma ina da ayyuka.” Ka nuna mini bangaskiyarka ba tare da ayyuka ba, ni kuma zan nuna maka bangaskiyata ta wurin abin da nake yi.
19
Ka gaskata cewa Allah ɗaya ne. To, da kyau! Ai, ko aljanu ma sun gaskata wannan, har da rawan jiki.
20
Kai wawa, kana son tabbaci cewa bangaskiya marar ayyuka banza ce?
Settings