Ishaya 10:21-23
21
Raguwa za tă komo, raguwar Yaƙub za su komo ga Maɗaukaki Allah.
22
Ko da yake mutanenka, ya Isra’ila, sun zama kamar yashin bakin teku, raguwa ce kurum za tă komo. A ƙaddara hallaka, mai mamayewa da mai adalci.
23
Ubangiji Maɗaukaki, zai sa hallakar da aka ƙaddara a kan dukan ƙasa ta faru.