Skip to content
Ibraniyawa 7:15-17

Ibraniyawa 7:15-17

15
Canjin nan a Dokar Allah ya ƙara fitowa fili da wani firist dabam wanda yake kamar Melkizedek ya bayyana.
16
Ya zama firist ne ba saboda ya cika wata ƙa’ida ta zama zuriyar Lawi ba, sai dai bisa ga ikon ran da ba a iya hallakawa.
17
Gama nassi ya ce, “Kai firist ne na har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options