Fitowa 29:43-46
43
a can kuma zan sadu da Isra’ilawa, in kuma tsarkake wurin da ɗaukakata.
44
“Ta haka zan tsarkake Tentin Sujada da bagaden, in kuma tsarkake Haruna da ’ya’yansa maza su yi mini hidima a matsayin firistoci.
45
Sa’an nan zan zauna a cikin Isra’ilawa, in kuma zama Allahnsu.
46
Za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu, wanda ya fitar da su daga Masar saboda in zauna a cikinsu. Ni ne Ubangiji Allahnsu.
Settings