Afisawa 2:16-18
16
A kan gicciye, Kiristi ya kawar da ƙiyayyar da take tsakaninmu da juna. Ya kuma kawo sulhu tsakaninmu da Allah.
17
Ya zo ya yi muku wa’azin salama; ku da kuke nesa da shi, ya kuma yi wa waɗanda suke kusa.
18
Gama ta wurinsa dukanmu za mu iya zuwa gun Uba ta wurin Ruhu guda.