Mai Hadishi 7:13-14
13
Ku lura da abin da Allah ya yi. Wa zai iya miƙe abin da ya tanƙware?
14
Sa’ad da al’amura suke tafiya daidai, ka yi farin ciki, amma sa’ad da suka lalace, ka tuna, Allah ne ya yi wancan shi ne kuma ya yi wannan. Saboda haka, mutum ba zai san wani abu game da nan gabansa ba.