Skip to content
Maimaitawar Shari’a 28:58-61

Maimaitawar Shari’a 28:58-61

58
In ba ku lura kuka bi dukan kalmomi wannan doka, waɗanda an rubuta a wannan littafi ba, ba ku kuma girmama wannan suna mai ɗaukaka da kuma mai banrazana na Ubangiji Allahnku ba,
59
Ubangiji zai aika da annoba masu zafi a kanku da zuriyarku, masifu masu zafi waɗanda za su daɗe, da mugayen cututtuka waɗanda ba sa kawuwa.
60
Zai kawo muku dukan cututtukan Masar da kuke tsoro, za su kuwa manne muku.
61
Ubangiji kuma zai kawo muku kowane irin ciwo da masifar da ba a rubuta a cikin wannan Littafin Doka ba, har sai an hallaka ku.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options