Maimaitawar Shari’a 28:15-20
15
Amma fa, in ba ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku ba, ba ku kuma lura kun bi dukan umarnansa da ƙa’idodin da nake ba ku a yau ba, dukan la’anan nan za su zo a bisanku, su kuma same ku.
16
Za ku zama la’anannu a birni da kuma a ƙauye.
17
Za a la’anta kwandonku da kwanon kwaɓan kullunku.
18
Za a la’anta ’ya’yan cikinku, haka ma hatsin gonarku, da ’ya’yan shanunku da ’yan tumakinku.
19
Za a la’anta ku sa’ad da kuka shiga da sa’ad da kuka fita.
20
Ubangiji zai aiko muku da la’ana, da ruɗewa, da damuwa cikin dukan abin da za ku yi, har ya hallaka ku, ku lalace da sauri saboda mugayen ayyukanku, domin kuma kuka rabu da ni.
Settings