Maimaitawar Shari’a 28:15-19
15
Amma fa, in ba ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku ba, ba ku kuma lura kun bi dukan umarnansa da ƙa’idodin da nake ba ku a yau ba, dukan la’anan nan za su zo a bisanku, su kuma same ku.
16
Za ku zama la’anannu a birni da kuma a ƙauye.
17
Za a la’anta kwandonku da kwanon kwaɓan kullunku.
18
Za a la’anta ’ya’yan cikinku, haka ma hatsin gonarku, da ’ya’yan shanunku da ’yan tumakinku.
19
Za a la’anta ku sa’ad da kuka shiga da sa’ad da kuka fita.
Settings