ข้ามไปยังเนื้อหา
2 Sama’ila 7:12-15

2 Sama’ila 7:12-15

12
Sa’ad da kwanakinka suka ƙare, za ka huta tare da kakanninka, zan tā da zuriyarka, na cikinka, zan kuma sa mulkinsa ya kahu.
13
Shi zai gina gida domin Sunana, zan kuwa kafa gadon sarautarsa har abada.
14
Zan zama Ubansa, shi kuma yă zama ɗana. Idan ya yi laifi, zan yi amfani da mutane in hukunta shi. Mutane ne za su zama bulalata.
15
Amma ba za a taɓa ɗauke ƙaunata daga gare shi yadda na ɗauke ta daga wurin Shawulu ba, shi wannan wanda na kawar daga gabanka.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options