Skip to content
2 Sarakuna 20:16-18

2 Sarakuna 20:16-18

16
Sai Ishaya ya ce wa Hezekiya, “Ka ji kalmar Ubangiji.
17
Lokaci yana zuwa da za a kwashe kome a fadanka da kuma dukan abubuwan da kakanninka suka tara har yă zuwa yau, a kai su Babilon. Ba abin da za a rage, in ji Ubangiji.
18
Za a kuma kwashe waɗansu daga cikin zuriyarka, na jiki da jininka waɗanda za a haifa maka, su zama bābānni a fadan sarkin Babilon.”
Settings

Reading style

Typeface

Font size 19px

Reading width 90 chars

Options