Skip to content
2 Sarakuna 13:20-21

Mutuwar Elisha da mu'ujizarsa bayan mutuwa

2 Sarakuna 13:20-21
20
Elisha ya mutu, aka kuma binne shi. To, mahara Mowabawa sun saba kawo hari a ƙasar Isra’ila a kowace bazara.
21
Wata rana yayinda waɗansu Isra’ilawa suke binne wani mutum, farat ɗaya sai ga mahara; saboda haka suka jefar da gawar mutumin a kabarin Elisha. Da gawar ta taɓa ƙasusuwan Elisha, sai mutumin ya farka, ya tashi ya tsaya da ƙafafunsa.
Settings

Reading style

Typeface

Font size 19px

Reading width 90 chars

Options