Skip to content
1 Sama’ila 18:12-14

1 Sama’ila 18:12-14

12
Shawulu ya ji tsoron Dawuda don Ubangiji yana tare da shi, amma Ubangiji ya riga ya bar Shawulu.
13
Saboda haka Shawulu bai yarda Dawuda yă zauna tare da shi ba, amma ya maishe shi shugaban sojoji dubu. Dawuda kuwa ya riƙa bi da su yana kaiwa yana kuma da tare da su.
14
A kome da Dawuda ya yi yakan yi nasara gama Ubangiji yana tare da shi.

Duba kuma

Sauran wuraren da Nassi ya faɗi haka

  • Farawa 39:23

    Mai gadin ba ya sa kansa game da kome da yake ƙarƙashin kulawar Yusuf, gama Ubangiji yana tare da Yusuf, ya kuma ba shi nasara a cikin dukan abin da ya yi.
    daga aya ta 14
  • 1 Sama’ila 16:18

    Ɗaya daga cikin bayin ya ce, “Na san wani yaro, ɗan Yesse na Betlehem, ya iya kiɗan molo, yana da hikima, shi kuma ya iya yaƙi. Ya iya magana, ga shi kuma kyakkyawa, Ubangiji kuwa yana tare da shi.”
    daga aya ta 12
  • Yoshuwa 6:27

    Ubangiji ya kasance tare da Yoshuwa, aka kuma san da shi a duk fāɗin ƙasar.
    daga aya ta 14
  • Mattiyu 28:20

    kuna kuma koya musu, su yi biyayya da duk abin da na umarce ku, kuma tabbatacce, ina tare da ku kullum, har ƙarshen zamani.”
    daga aya ta 14
  • Farawa 39:2

    Ubangiji kuwa yana tare da Yusuf, Yusuf kuwa yi nasara, ya zauna a gidan mutumin Masar maigidansa.
    daga aya ta 14
  • Farawa 39:3

    Sa’ad da maigidansa ya ga cewa Ubangiji yana tare da Yusuf, kuma cewa Ubangiji ya ba shi nasara a kome da ya yi,
    daga aya ta 14
  • 1 Sama’ila 18:15

    Da Shawulu ya ga yadda yake cin nasara, sai ya ji tsoronsa.
    daga aya ta 12
  • 1 Sama’ila 18:29

    sai Shawulu ya ƙara jin tsoron Dawuda har ya zama maƙiyinsa a dukan sauran rayuwarsa.
    daga aya ta 12
  • 2 Sama’ila 5:2

    A dā da Shawulu yake sarauta a bisanmu, kai ne kake bi Isra’ilawa zuwa yaƙe-yaƙensu. Ubangiji kuwa ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayi mutanena Isra’ila, za ka kuma zama sarkinsu.’ ”
    daga aya ta 13
  • 1 Sama’ila 10:7

    Da zarar waɗannan alamu sun cika, sai ka aikata duk abin da kana iya yi gama Allah yana tare da kai.
    daga aya ta 14
  • Ayyukan Manzanni 18:10

    Gama ina tare da kai, ba kuma wanda zai fāɗa maka ya cuce ka, domin ina da mutane da yawa a wannan birni.”
    daga aya ta 14
  • Mattiyu 1:23

    “Ga shi budurwa za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, kuma za a kira shi Immanuwel” (wanda yake nufin “Allah tare da mu”).
    daga aya ta 14
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options