1 Sarakuna 21:13-14
13
Sa’an nan ’yan iska biyu suka zo, suka zauna ɗaura da shi, suka kawo zarge a kan Nabot a gaban mutane, suna cewa, “Nabot ya zagi Allah da sarki.” Saboda haka aka ɗauke shi waje da birnin, aka jajjefe shi da dutse har ya mutu.
14
Sa’an nan suka aika wa Yezebel. “An jajjefe Nabot, ya kuma mutu.”