1 Korintiyawa 15:24-26
24
Sa’an nan sai ƙarshen ta zo, sa’ad da zai miƙa wa Allah Uba mulki, bayan ya hallaka dukan sarauta, mulki da iko.
25
Gama dole yă yi mulki har sai ya sa dukan abokan gābansa a ƙarƙashin ƙafafunsa.
26
Abokin gāba na ƙarshen da za a hallaka kuwa, shi ne mutuwa.