1 Korintiyawa 14:37-40
37
In wani yana tsammani shi annabi ne, ko yana da baiwar ruhaniya, bari yă gane cewa abin da nake rubuta muku umarnin Ubangiji ne.
38
In ya ƙi kula da wannan, shi ma sai a ƙi kula da shi.
39
Saboda haka ’yan’uwana, ku yi marmarin yin annabci, kada kuma ku hana magana da harsuna.
40
Sai dai a yi kome daidai da kuma cikin tsari.
Settings